Kowane mutum na da hakkin kasancewa a cikin ja-gorancin harkokin jama'a na ƙasarsu, ko shi da kansa ko ta hanyar aika wakilansa waɗanda ya zaba cikin ƴanci.
Kowane mutum na da hakki a cikin sharaɗin daidai-wa-daida ya sami halin a ɗaukaka shi ya kama ragamar tafiyar da waɗansu ayyukan ƙasarsu na kula da harkokin jama'a.
Kowane mutum na da hakkin ya sami isasshen halin da zai rayu da shi domin ya kiyaye lafiyarsa da shi da iyalinsa, da jin dadin rayuwarsu, ya kuma mallaki halin tabbatar musu da abinci da tufafi da mahalli da magani daga likita da sauran abubuwan kyautata rayuwa waɗanda suke buƙata.